Daga Othman Ibn Affan (Allah ya yarda da shi), Manzon Allah (Sallallahu alaihi wa sallam) ya ce: “Wanda ya yi cikakkiyar alwala, zunubansa suna fita daga jikinsa har zuwa inda suke fita daga ƙarƙashin yatsunsa.”
(An rawaito daga Muslim a cikin Sahih dinsa lamba 245)
A cewar Abū Huraira (Allah ya yarda da shi), Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce: “’Umrah zuwa ga ‘umrah tana gafartawa ga abin da ke tsakanin su, kuma aikin Hajji da tsoron Allah ba shi da wani sakamako illa Aljanna.”
(An rawaito daga Bukhari cikin Sahih dinsa lamba 1773 da Muslim cikin Sahih dinsa lamba 1349)
Daga Abou Houreira (Allah ya yarda da shi), Manzon Allah (salallahu alaihi wa sallam) ya ce: « Ku kalli wainda suke ƙasa da ku kuma kada ku kalli wainda suke sama da ku, wannan domin kada ku raina ni’imar Allah a kanku ».
(An ruwaito daga Muslim a cikin Sahih ɗinsa lamba 2963)
A cewar ‘Abdallah ibn Abi Qatada (Allah ya yarda da shi), Manzon Allah (Sallallahu alaihi wa sallam) ya ce: « Idan ɗayanku yana sha, kada ya yi numfashi cikin abin sha; idan yana yin fitsari kada ya taɓa al’aura da hannun dama, kuma idan yana tsabtace kansa (bayan ya yi bukatarsa), kada ya yi amfani da hannun dama. »
[Sahih al-Bukhari 5630]
Daga Abou Houreira (Allah ya yarda da shi), Manzon Allah (Sallallahu alaihi wa sallam) ya ce: « Ku tuna da wadda ke yankar da jin daɗi » ma’ana yana nufin mutuwa.
(An rawaito ta Tirmidhi cikin Sunnan sa lamba 2307 kuma Sheikh Albani ya tabbatar da ingancinsa cikin gyaran Sunnan Tirmidhi)